Yadda masu kuɗi ke lalata ƴaƴan talakawa a Kano – Daurawa

Shugaban Hukumar Hizba ta jihar Kano, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya bayyana takaici kan yadda tarbiyya ke ƙara taɓarɓarewa tsakanin al’umma a jihar.

Malamin ya bayyana hakan ne a hirarsa da BBC.

Kano da ke arewacin Najeriya jiha ce mai yawan al’umma kuma cibiyar kasuwanci a yankin.

Duk da cewa akwai ƙabilu da yawa da suke zaune a jihar amma kasarin al’ummarta mabiya addinin musulunci ne.

Wannan ya sanya koyarwa da al’adu na addinin musulunci ke da matuƙar tasiri, lamarin da ya sanya gwamnatin jihar ta kafa hukumar Hisba wadda aka ɗora wa alhakin tabbatar da cewa al’umma na bin dokoki addinin na Musulunci.

Sai dai a kwankin baya-bayan nan ayyukan hukumar ya riƙa haifar da cecekuce da muhawarori.

Na baya-bayan nan shi ne yanda hukumar ke takun-saƙa tsakanin ta da masu wallafa bidiyo a shafukan sada zumunta, musamman tiktok.

Related Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

© 2024 Mikiya - WordPress Theme by WPEnjoy
Danna Nan Ka Kalli Bidiyon 👈
error: Content is protected !!